Min menu

Pages

Gwamnatin Najeriya Zata Samarwa Matasa 20,000 Masu Digiri Aiki Mai Tsoka, Da Za'a Dinga Biyansu Kamar Yadda Ake Biyan Ma'aikata Masu Digiri

 Gwamnatin Najeriya Zata Samarwa Matasa 20,000 Masu Digiri Aiki Mai Tsoka, Da Za'a Dinga Biyansu Kamar Yadda Ake Biyan Ma'aikata Masu Digiri



Gwamnatin Najeriya karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari, zata fara daukan matasa masu digiri ai a Gobe Talata.


Gwamnatin Najeriya ta kirkiri shirin ne da nufin samarwa matasa 'yan Najeriya da suka kammala digiri har mutum 20,000 aikin yi a wasu bangarorin gwamnati da kamfanoni a fadin kasa.


Rahoto ya nuna cewa aikin matasan (yan kasa da shekara 30) zai kwashe watanni 12, kuma za'a basu cikakken albashin masu digiri.


Gwamnatin tarayya na fatan aikin zai taimaka wajen kimtsa matasan da suka kammala karatu domin gobensu da kuma muhallan aiki da zasu iya tsintar kansu nan gaba.

Comments