Min menu

Pages

Hukumar NCDC Ta Gargadi Musulmai Game Da Yawon Babbar Sallah, Don Kaucewa Kamuwa Da Cutar Corona A Karo Na Biyu

 Hukumar NCDC Ta Gargadi Musulmai Game Da Yawon Babbar Sallah, Don Kaucewa Kamuwa Da Cutar Corona A Karo Na Biyu



Yayin da musulmai masu ke shirin bikin sallah babba a mako mai zuwa, Cibiyar Kula da Cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta yi gargadi game da tafiye-tafiye a lokacin bukukuwan sallah.


Shugaban NCDC na Sashin Sadarwa, Dakta Yahya Disu, shi ne ya bayar da wannan gargadin a ranar Laraba yayin shirin karin kumallo na gidan Talabijin din Channels. 


Disu ya ce karo na biyu na annobar Corona ta fara ne a Nijeriya saboda mutane sun yi tafiya don Kirsimeti a Disambar da ta gabata. 


Don haka, ya bukaci 'yan Nijeriya da su guji tafiye-tafiye marasa mahimmanci a lokacin bukukuwan sallah na mako mai zuwa.


Ya bukaci shugabannin addinai da su wayar da kan mabiyansu a kan wajabcin kiyaye ka’idojin Korona domin kiyaye karuwar yaduwar cututtuka. 


Disu ya ce: "Mafi mahimmanci, sallah tana zuwa, lokacine da mutane ke tafiye-tafiye kuma hakan na kara hadari ga kauyuka, a sassa daban-daban na kasar. 


"Don haka, muna bukatar fadakar da mutane: ba sa bukatar tafiye-tafiye idan ba dole ba ne, za ku iya yin biki a inda kuke. 


A lokacin sallah, muna zuwa masallaci adadi mai yawa kuma wannan shine lokacin da ya kamata mu kiyaye.

Comments