Min menu

Pages

Za mu baiwa 'yan Luwadi da 'yan Madigo cikakkiyar kulawa~Joe Biden

 Za mu baiwa 'yan Luwadi da 'yan Madigo cikakkiyar kulawa~Joe Biden



Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya bayyana cewa Gwamnatin sa zata baiwa 'yan Luwadi da 'yan Madigo 'yancin gudanar da harkokin su kamar sauran jama'a.


Biden ya kara da cewa, 'yan Luwadi da 'yan Madigo mutane ne kamar kowa, saboda haka suna da damar yin irin rayuwar da su ke so.


Saboda haka dan Luwadi  ko 'yar madigo suna da damar aure ko yin soyayya da wanda su ke so don gudanar da harkokin su.


Biden ya bayyana hakan ne da yammacin yau Litinin albarkacin ranar kyamar 'yan luwadi da 'yan madigo



Comments