Min menu

Pages

RAN MAZA YA BACI:-Shugaban kasar Turkiyya yayi kira ga shugabannin kasashen duniya suyi Tur da Allah wadai ga kasar isra'ila kan zaluncin da suke yiwa musulman palasdine



Shugaban kasar Turkiyya Raceb Tayyip Erdogan ya ayyana kasar Isra'ila a zaman kasar 'yan ta'adda


Shugaban kasar Turkiyya Raceb Tayyip Erdogan ya yi kira ga kasashen musulmai na duniya da su yi tir da Allah-wadai ga kasar Isra'ila akan iri zaluncin da su ke yi wa musulmai Palasdiwa a cikin wannan wata na Ramadan.


Erdogan ya kara da cewa, baza su taba zura ido suna gani ana cin zarafin musulmai na Palasdiwa ba.


Daga karshe Erdogan ya roki Allah ya isar ma 'yan uwa musulmi da aka ci zarafin su kawo yanzu.

Comments