Min menu

Pages

SALON SATAR KUDIN MUNE.... GARKUWA DA DALIBAI

 


Babban Dalilin Da Yasa Ake Satar Dalibai a Nigeria. Sirrin boye ya fito fili...



Nigeria kasa ce gurbatacciya, da ta gurbata da gurbatattun shugabani marasa tsoron Allah. Abubuwan da shugabannin kasar nan keyi ya wuce hankalin mai hankali ya kuma wuce duk tunanin mai tunani.




Duk wani shashe na kungiya, ma aikata ko company, ta batgaren gwamnati da wanda ba gwamnati ba duk yawancin mutanen da ke shugabatar wajen son zuciya ne kawai ke gabansa ba al'ummar da yake wakilta ko shugabanta ba.




Abin har lalacewar takai a samu mugayen mutane su tsiro da wata mummunar manufa akan Dalibai dake karatu a makarantu saboda rashin imani da manta Allah.




Wannan satar daliban da akeyi bafa wasu kidnappers, gwamnonin jaha sune kattan kidnappers din. To kuwa a haka ya za ayi ace min cigaba da irin wadannan gurbatattun mutane.




Asirin gwamnan wata jaha tamu dake nan Arewa ya tonu dalilin kudin fansar da suka diba suka baiwa wadanda aka sa suka sace yaran suke ganin an kwaresu a zunzurutun kudin da aka samu.



Sun so a kara masu wani kaso gwamnatin taki saboda dama yadda akace za a basu shine 30% a cikin kudin.




Kuma ikon Allah haka din aka basu amma da yake dukkansu barayin zaune ne da gwamnatin da wadanda take sawa suyi aikin sai suka ga ya kamata a kara masu wani abu tunda dawan tayi nama.




To dama harkace ta rashin amana, sai fa suka fito Suna ta yamadidi da ton silili a boye suna revealing secret din.




To a takaice dai babban Dalilin da yasa gwamnati ke satar yara Daliban makaranta shine, idan suka sa aka sace su. Sai su ware kudi masu tsoka suce sune kudin fansar da kidnerphers sukace a bada.




Bayan 'yan kwanaki sai suce sun bada kudi sun karbosu, sai su biya wadanda suka sa suyi masu aikin kudin da sukai yarjejenita dasu. Su sallamesu. 




Wadannan zunzurutun kudin kuwa sai su karkatar dasu daga baitil malin gwamnati zuwa asusun aljihunsu. A gaba idan tenure dinsu ta kare duk wani gwamna da zai hau yayi bincike, zai ga an ware miliyoyin kudi an fanso yara.




Kunga ay ba maganar binciken wadannan kudin tunda a rubuce ga abinda akayi dasu....



Jama'a a takaice inaso kusani salon satar kudin gwamnatine ake fakewa da satar daliban makarantu, don haka ya kamata a fito a yaki wadannan gurbatattun gwamnonin, masu fakewa da guzuma Suna harbin karsana



Allah Yayi mana maganinku

Comments