Min menu

Pages

Kishiyarta ta kone ta kurmus har lahira

 Kishi ko hauka?



Kishiyarta ta kone ta kurmus har lahira.


Wata kishiya ta aikata mummunan aiki kan amaryar da aka kawo mata a matsayin abokiyar zama.


Inda ta saka mata wuta ta koneta kurmus har lahira.


Duka duka auren kwana hamsin da yinsa amma kishi yasa ta kone ta.


Inda ta kulleta a daki kuma ta bankawa dakin wuta lamarin daya jawo konewar tata kenan.


Amaryar da aka kone har asalin jihar Katsina ce kuma sunanta Fatima.


Yau za ayi jana'izar ta insha Allahu.

Lamari na kishi yana saka mata da yawa fita daga cikin hankalinsu har su aikata mummunan aiki wanda daga karshe kowa zaizo yana yin dana sani.


Ya kamata mata suna kaiwa zuciya nesa suna hakuri da junansu.

Comments