Min menu

Pages

Abubuwa guda shida daya kamata ku sani akan sabon shugaban yan sanda Zanna Muhammad.

 Abubuwa guda shida daya kamata ku sani akan sabon shugaban yan sanda Zanna Muhammad.



Waye Zanna Muhammad

Dan asalin wacce jihar ne

Wanne mataki ne dashi a karatu

Shugaban kasa Muhammed Buhari ya nada mataimakin shugaban yan sanda na kasa amatsayin shugaba na yan sandan tun bayan gama adadin shekarun da tsohon shugaban yan sandan yayi.

To saidi yanada kyau mutane su san wadannan abubuwan guda shida a game da sabon shugaban yan sandar wanda zamu lissafo a kasa.

- An haifi mai girma sabon shugaban yan sandar a watan November ranar ashirin da shida a shekarar 1962.

- Ya bachelor degree dinsa a wata jami'a a garin Jos jihar Plateau.

- Sunansa ya fito a cikin jerin yan sanda a ranar sha biyar ga watan uku na shekarar 1988.

- Ya gama koyon aikin yan sanda a gurin koyarwa a Kaduna daga nan sai aka tura shi jihar Borno inda yayi shekara daya a wata division dake garin Biu cikin jihar ta Borno.

- Ya samu mukamin kwamishinan yan sanda a Jihar Delta da kuma Zamfara kafin daga karshe ya samu mukamin mataimaki (AIG)

- A karshe dai ya samu kansa cikin tawagar masu bincike game da harkar danyen mai a lokacin Jonathan sannan dan jihar Borno ne.

Mutane da dama daga gurare sun bayyana shugaban yan sanda Zanna Muhammad amatsayin dan sanda mai riko da gaskiya cikin ayyukansa.

Hakan yasa lokacin da akaji shugaban kasa Muhammed Buhari ya fitar dashi a matsayin shugaban yan sanda na kasa mutane keta addu'a na ganin an samu ci gaba sosai.


Comments