Min menu

Pages

Kabilar da suke aske gashin kansu idan dan uwansu ya mutu.

Kabilar da suke aske gashin kansu idan dan uwansu ya mutu.



Assalamu alaikum yan uwa barkanmu da wannan lokacin ya kuke ya hakurin kasancewa tare damu?


Hakika muna matukar jin dadin yadda kuke kasancewa tare damu,kuma muna godiya sosai da sosai.


A yau cikin shirin namu munzo muku ne da labarin wata kabila mai abin mamaki wacce dole sai yan gidan sun aske gashin kansu daga zarar wani dan uwansu ya mutu, bawai yan gidan bane su kadai zasu aske gashin kan nasu ba a'a duk wani jinin mamacin dole ne sai ya aske kansa idan har akayi mutuwa a cikin danginsu.


Kowacce kabila sunada wani abu da suke gabatarwa wanda idan mutum ba'a cikin kabilar yake ba sai yaji abin wani iri.


Kabilar hindus suna gabatar da wani abu na al'ada wanda suke kira MUDAN,  suke aske gashin kansu duk lokacinda dan uwansu ya mutu dan nuna jimami da kuma jin zafin mutuwar dan uwan nasu.


Kuma wannan al'ada ta jima ana yinta a wasu yankunan na kasar India.



Comments